Haɗin kai yana faruwa tsakanin al’ummomi masu ra’ayi ɗaya, ko guri ɗaya, kuma yana tare da taimakon juna.

Al’ummar Nijar tana buƙatar goyon bayan Faransa.

Kamar yadda ƙungiyar raya ƙasashe masu tasowa ta majalisar ɗinkin duniya ta bayyana, Nijar tana ɗaya daga cikin ƙasashen da suke a bayan fage a fannin jin daɗin rayuwa.

Duk da Nijar tana da wadatar mutane da al’adun gargajiya, al’ummar tana fuskantar talauci, da rashin ruwa, da na abinci, da na tabbatar da horo da magungunna.

Wasu mutanen ƙasar waɗanda suka samu horo, ƙwararru kuma masu niyya, suna kokowa har kullum don kyautata rayuwar al’ummomin karkara da na birni. Waɗanga mutanen da ke taimaka wa al’ummomi wajen ci-gabansu, suna tare da al’ummomin, tunda harsunansu da tabi’unsu da ka’ idojin zamankakewarsu, da kuma aƙidansu, ɗaya ne. Sun fi kowa sanin abubuwan da ya kamata a gudanar na ci-gaba tare da al’ummomin domin jin daɗinsu.

Abinda ba su da galihu sune hanyoyin samun kuɗi, da tallafin ɗabi’a

Faransawa suna iya taimaka wa al’ummar Nijar.

Faransa tana ɗaya daga cikin ƙasashe na sahun gaba a fannin jin daɗin rayuwa. Mazauna cikinta suna da abinci, ilimi, lafiya da ruwa.

Yana da fa’ida daga sadaukarwar mutane masu dacewa a fagen zamantakewa, kiwon lafiya ko aikin ilimi waɗanda ke gwagwarmaya yau da kullun game da wariya, rashin adalci, kaɗaici da nuna wariya.

Sanya wani sashi na wannan dukiyar da wannan ƙwarewar a hidimar ci gaban ƙasar Nijar shi zai bayar da gudummawa ga kyakkyawar rayuwa da ci gaba mai dorewa.

 

Dans cette rubrique