Unguwa ce a Kewayen Yamai inda yaran talakkawa da yawa masu fama da talauci ba su samu shiga makarantar boko ba. A nan ne wani ‘’huroje’’ da ya fara aiki a shekarar 2002 yake tara waɗanga yara ta hanyar wata ƙungiyar matan unguwar, sai ya ba su horon shekara guda don su samu shiga cikin sauran makarantun gwamnati a shekara mai zuwa.
Makarantar « fata » ta tsaida ayyukanta tsakanin 2013 da 2016.
An sake kafa sabon aji a watan Oktoba 2017. Akwai ƴan makaranta 31, ƴan mata 19 da ƴan maza 12, an samu damar yin wannan aiki da kudaden da AECIN ke biya. Makarantar yanzu dai a sa mata sunan Mahamadu Saidu, wanda ya kafa ta. Mai gudanar da ayyukan ta nuna da cewa inda ana son a yaki rishin zuwa makaranta na yara, to sai an kafa tsarin cin abinci a makarantar da rana. Saboda haka AECIN ta tara kuɗi yin starin.
A shekara ta 2018-2019, an koma makaranta ran 1 ga watan oktoba, ɗalibai 30 ke akwai, ’yan mata 8 da ‘yan maza 22. ’yan mata ba su da yawa saboda ƙanana ne, shekarunsu ba su isa su shiga makarantar unguwa ba. An yi wani annoba ta ƙarimbau a watan Janairu 2019, ta kama mai gudanar da ayyukan makarantar, amma yanzu kome na zuwa daidai. Lokaci ne mafi wuya a shekara don yanayi, kuma farashin abinci yana hawa. Hakanan an kawo ruwa kusa da aji wanda zai ba da izinin noman lambun a cikin makarantar.
An rufe ajin wani lokaci a shekarar 2020 saboda takurawar da aka sanya don shawo kan cutar COVID. An fara karatu na shekarar 2020/2021 a ranar 12 ga watan Oktoba, 2020. Rukunin daliban ya hada da ‘yan mata 15 tare da maza 15 wadanda aka zaba cikin dalibai hamsin. A lokacin bazara na 2021, ’yan mata goma sha huɗu da maza goma suka samu shiga aji na 4 na firmare, sauran ɗalibai shida sun samu shiga aji na biyu ko na uku na firmare.
A watan Oktoban 2021, ajin Mahamadu Saidu ya bude kofofinsa ƙumshe da dalibai 24 da suka hada da mata 7 da maza 17, a gundumar Tallague ta Yamai, za a kara yawan adadin yara mata ya zama ɗaya da na maza. Ajin a wannan shekara an sanya masa fitulun hasken rana guda 40. Wannan yana bawa ɗalibai da iyalansu damar samun tushen haske.
AECIN ke daukar tallafin kudaden ajujuwan karatu da na abinci.
